Thursday, 14 November 2013

Najeriya na neman sulhu da Boko Haram

Gwamnatin Najeriya ta ce abin da ta sa a gaba shi ne kokarin sulhuntawa da 'yan kungiyar da wasu ke kira Boko Haram ba maganar gurfanar da su gaban kuliya ba. Mahukunta a Najeriyar sun ce ba a maganar shari'a sai sulhu ya gagara. Gwamnatin dai na mai da martani ne dangane da matakin da majalisar dinkin duniya ta dauka na sanya 'yan kungiyar Jama'atu Ahlis sunnah lidda'awati wal jihad da wasu ke kira Boko Haram a sahun masu aikata laifukan yaki idan aka tabbatar da aikata laifukan da ake zarginta da yi. Wannan matakin zai ba da kafar gurfanar da duk wani dan kungiyar da ake zargi a kotun hukunta laifukan yaki ta duniya da ke Hague.

No comments:

Post a Comment