Monday, 11 November 2013
Akalla mutane 7 sun mutu sakamakon fadan da aka fafata da ‘yan Bindiga a Najeriya
Rahotanni daga jihar Kano da ke yankin Arewa maso yammacin tarayyar Najeriya na nuna cewar an yi dauki-ba-dadi tsakanin Soji da wasu ‘yan Bindiga da aka zarga da kokarin kai harin kunar bakin Wake a Kano da Abuja.
‘Yan Bindigar dai sun bayyanawa Kamfanin dillancin labarai na AFP cewar akalla Soji Biyu 2 da wasu ‘yan Bindigar Biyar 5 sun mutu a wannan fafatawa da aka yi.
Mai magana da Yawun Sojin Najeriya a yankin Captain Iweha Ikedichi, ya bayyana cwar bayannan sirrin da suka samu sun nuna masu cewar ‘yan Bindigar na kokarin kammala shirin kaddamar da wani harin ne a Abuja da Kano kuma Sojin sun gano jibgin Makamai a wannan harin da suka kai.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)

No comments:
Post a Comment