Sakataren kudi na kungiyar Miyatti Allah ta Fulani makiyaya reshen jihar Pilato Malam Salihu Jauro ya ce lamarin ya faru ne a kauyen Sit dake tsakanin Pankshin da Langtan ta arewa.
Makiyayan na neman mahukunta da su basu cikakken tsaro tare da dabbobinsu.
A mafi yawan lokuta dai satar shanu na haddasa rikicin kabilanci a yankin.
Jihar Pilato ta sha fama da rikicin kabilanci da addini tsawon shekaru 14.
No comments:
Post a Comment